Kafafen watsa labaran sun jiyo wani jami'in kamfanin jiragen sama na Aseman na Iran din yana fadin cewa jirgin samfurin ATR 72 ya fado ne a dutsen Dena kusa da garin Semiron na lardin Isfahan saboda munin yanayi.
Wasu rahotanni sun ce jirgin dai wanda ya taso daga filin jirgin sama na Mehrabad da ke birnin Tehran yana dauke da fasinjoji 60 a cikinsa, matukan jirgi biyu da kuma sauran ma'aikata da jami'an tsaro.
Shugaban hukumar agajin gaggawa ta kasar Iran Murtadha Sulaimani ya bayyana cewar tuni aka aike da wata tawaga ta jami'an ba da agaji su 20 zuwa yankin da abin ya faru don ci gaba da gudanar da bincike da kuma yiyuwar ba da agaji, sai dai ya ce har ya zuwa yanzu an gagara tura jirage masu saukan ungulu na agaji zuwa yankin sakamakon munin yanayin.